Rundunar sojan Masar ta hambarar da Mohammed Morsi daga karagar mulki
2013-12-09 16:15:12
cri
13afirka
Ranar 3 ga watan Yuli, rundunar sojan kasar Masar ta sanar da hambarar da shugaba Mohammed Morsi daga karagar mulki, saboda a cewar su ya gaza shawo kan matsalolin da ake fuskanta a kasar ta Masar. An kuma rantsar da babban alkalin kasar Masar Adli Mansour a matsayin sabon shugaban kasar na rikon kwarya. Daga nan ne kuma tashe-tashen hankula suka kara tsananta a kasar ta Masar.