Ranar 26 zuwa 27 ga watan Maris, shugabannin kasashen BRICS sun yi ganawa a tsakaninsu karo na 5 a birnin Durban na kasar Afirka ta Kudu. Babban taken ganawar shi ne hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen BRICS da na Afirka domin habaka ci-gaba da dunkulewa, da kuma bunkasar masana'antu. mahalarta taron sun zurfafa tattaunawarsu kan yadda za a inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashen BRICS da na Afirka.