in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar kasashen BRICS zai inganta bunkasuwar tattalin arzikin Afirka ta Kudu, in ji shugaban kasar
2013-03-20 10:55:23 cri
Daga ranar 26 zuwa 27 ga wata, za a kira taron ganawar shugabannin kasashen BRICS karo na biyar a Durban, birnin tashar jiragen ruwa na kasar Afirka ta Kudu.

A ranar 19 ga wata, shugaban kasar Jacob Zuma ya bayyana cewa, hadin gwiwar tsakanin kasashen BRICS zai inganta bunkasuwar tattalin arzikin kasar, da kuma samar da karin guraben aikin yi.

Yayin babban taron horaswa da ilimantar da ma'aikatar matasa ta kasashe renon Ingila da aka kira a Pretoria, babban birnin kasar Afirka ta Kudu, shugaba Jacob Zuma ya nuna cewa, gaba daya, yawan kudin da aka samu wajen samar da kayayyaki na kasashen BRICS ya kai kashi 25 bisa dari na dukkan kasashen duniya, kana kasashen na da yawan mutanen da suka kai kashi 43 bisa dari na duk duniya, yayin da kuma ajiyar kudin musanya da ke wajen wadannan kasasahen BRICS ya kai dallar Amurka biliyan dubu 44.

Bisa wadannan dalilai, hadin gwiwar kasashen BRICS din zai samar da isassun guraben aikin yi ga matasa, da kuma biyan bukatunsu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China