in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan za a samu ci gaban hadin gwiwa kan hada-hadar kudi tsakanin kasashen BRICS
2013-03-20 21:09:27 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci taron shugabannin kasashen BRICS karo na biyar da za a yi a birnin Durban na kasar Afirka ta Kudu. A ranar Laraba 20 ga wata, mataimakin ministan harkokin wajen Sin Ma Zhaoxu ya bayyana cewa, Sin na fatan za a samu ci gaba a fannonin bude bankin bunkasuwa na BRICS, da kafa asusun musayar kudaden kasashen waje, da sauran muhimman ayyuka da suka shafi hakan.

Ma, wanda ya yi wannan tsokaci yayin taron 'yan jaridu na gida da na waje, ya bayyana cewa, za a gudanar da taron birnin Durban a ranar 26 da 27 ga wata. Yanzu kasashen BRICS suna yin shawarwari kan batun kafa asusun musayar kudaden kasashen waje, yayin da hukumomin kudi na wadannan kasashe suke nazari kan hakikanin abubuwa da suka shafi wannan batu.

Yayin dai wannan taro, shima mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin, Zhai Jun ya bayyana cewa, za a yi taron yin shawarwari tsakanin shugabannin kasashen BRICS da na kasashen Afirka a yayin taron na Durban dake tafe. Ana fatan dai wannan taro zai karfafa shawarwari, da hadin gwiwa tsakanin kasashen BRICS da na nahiyar Afirka, tare da kara karfin wakilci na kasashe masu karfin bunkasar tattalin arziki, da kasashe masu tasowa cikin harkokin duniya. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China