in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Birtaniya sun fidda sanarwar hadin gwiwa kan batun Afghanistan
2016-12-22 10:59:03 cri
A ran 20 ga wata ne, aka bude taron shawarwari tsakanin kasar Sin da kasar Birtaniya bisa manyan tsare-tsare karo na 8 a birnin London, bayan gudanarwar taron, bangarorin biyu sun fidda wata sanarwa cikin hadin gwiwa kan batun Afghanistan, inda suka jaddada cewa, kasashen Sin da Birtaniya za su ci gaba da goyon bayan gwamnati da al'ummomin jamhuriyyar Islama ta kasar Afghanistan. Zaman lafiya da tsaron kasar Afghanistan yana da muhimmanci ga kasashen Sin da Birtaniya, a saboda haka, kasashen biyu za su hada kai da sauran kasashen duniya domin ba da gudummawar raya kasar Afghanistan.

Haka kuma, cikin sanarwar, bangarorin biyu sun jaddada cewa, ya kamata al'ummomin kasar Afghanistan su kasance a kan gaba kana su warware ricikin kasarsu da kansu ta hanyar siyasa. kana, a matsayinta na wakilan din-din-din a kwamitin sulhu na MDD, kasar Sin da kasar Burtaniya za su ci gaba da nuna goyon baya ga gamayyar kasa da kasa domin taimaka wa rundunonin sojojin kasa ta Afghanistan cimma burinsu na shimfida zaman lafiya a kasar.

Bugu da kari, kasashen Sin da Burtaniya sun cimma daidaito na yin hadin gwiwa da gwamnatin kasar Afghanistan, domin taimaka wa kasar Afghanistan taya hukumominta da ababan more rayuwa ta hanyar hadin gwiwar masanan kasashen uku. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China