in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira da a kara azama kan samun zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaba a Afghanistan
2016-09-15 13:29:16 cri

Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya yi kira ga kasashen duniya da su ci gaba da bai wa gwamnatin kasar Afghanistan tallafi da goyon baya, a kokarin gaggauta wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaban kasar.

A jiya Laraba ne dai kwamitin sulhun ya shirya wani taro kan batun Afghanistan, tare da zartas da wata sanarwar shugaba, inda ya kalubalanci sassa daban daban da su hada kai wajen samar wa jama'ar Afghanistan kyakkyawar makoma ta zaman lafiya da wadata.

A cikin jawabinsa a yayin taron, Wu Haitao ya ce, a Afghanistan sulhunta al'umma yana gaban komai. Kuma ya kamata sassa daban daban na kasar su mayar da makomar kasarsu, da kuma moriyar jama'arsu a gaban kome, su kuma koma ga teburin shawarwarin zaman lafiya cikin hanzari.

Kaza lika ya zama wajibi kasashen duniya su ci gaba da yin kokari, wajen goyon bayan aikin sulhu tsakanin dukkan bangarorin kasar ta Afghanistan, a karkashin shugabancin jama'ar kasar, ko a kai ga cimma nasarar sulhu a wannan kasa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China