Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yau Jumma'a cewa, ministan harkokin waje da yin hadin gwiwa da kasa da kasa na Jamhuriyar demokiradiyar Kongo mista Raymond Tshibanda zai kawo ziyarar aiki nan kasar Sin daga ranar 29 ga watan Yuli zuwa ranar 1 ga watan Agusta.
Mr Lu ya ce, Tshibanda zai kawo wannan ziyara ce bisa gayyatar takwaransa na kasar Sin Wang Yi. (Tasallah)