in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron koli na kungiyar kasuwar bai daya ta gabashi da kudancin Afirka
2014-02-27 14:55:59 cri

An bude taron koli na kungiyar kasuwannin bai daya ta gabashi da kuma kudancin Afirka karo na 17, a birnin Kinshasa, babban birnin kasar Kongo(Kinshasa). Taron wanda zai gudana daga ranar 26 zuwa 27 ga watan nan, ya samu halartar shugabanni da wakilai na kasashen mambobin kungiyar 19.

Abubuwan da aka sanya gaba yayin wannan taron koli, sun hada da kaddamar da yankin cinikayya cikin 'yanci na kungiyar, da sa kaimi ga bunkasuwar kawancen kula da harkokin harajin hukumomin kwastan.

Haka zalika za a gudanar da shawarwari tsakanin bangarori uku na kungiyar, da kungiyar gamayyar gabashin Afirka, da kungiyar gamayyar raya kudancin Afirka. Sai kuma batun kyautata tsaro da zaman lafiya, da bunkasa samar da ababen more rayuwar al'umma, da aikin gona, da muhalli da dai sauran muhimman batutuwa.

A wannan karo shugaban kasar Kongo(Kinshasa) Joseph Kabila, ya maye gurbin takwaransa na kasar Uganda Yoweri Museveni, wanda a baya, shi ne ke jagorantar kungiyar kasuwar bai daya ta gabashi da kuma kudancin nahiyar ta Afirka.(Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China