in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Watakila wani babban jam'in dakarun dake adawa ga gwamnatin Kongo(Kinshasa) sun buya a Uganda
2013-11-20 11:15:47 cri
A ranar 19 ga wata, wani mai liken asiri na kasar Uganda ya bayyana cewa, shugaban dakarun mai dauke da makamai da ke adawa ga gwamnatin Kongo(Kinshasa) Makenga ya buya a kasar Uganda, kuma sojojin Uganda sun ba da kariya gare shi.

Bisa labarin da kafofin yada labaru na kasar Kogo(Kinshasa) suka bayar, an ce, a wannan rana, wannan jami'in liken asiri da ba ya son fayyace sunansa, ya bayyana a birnin Goma da ke yankin gabashin kasar cewa, yanzu, Makenga ya buya a birnin Kampala, babban birnin kasar Uganda. Yana mai cewa, sojojin kasar Uganda sun ba da tabbaci game da tsaronsa. Amma, bisa yin la'akari da batun tsaro, ba ya fayyace inda yake zama ba.

A matsayin shugaban dakarun M23, a karshen shekarar bara, M.D.D. da Amurka sun sanya sunansa cikin takardar yin takukumi, kuma yanzu, gwamnatin Kongo(Kinshasa) tana kokarin neman shi.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China