in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An cimma matsaya game da aikin mayar da 'yan gudun hijirar Kongo Kinshasa zuwa gidajensu
2014-05-01 16:28:03 cri
Jami'an daga kasashen Uganda, da Kongo Kinshasa, da na hukumomin MDD sun bayyana cimma matsaya guda, game da shirin sake ci gaba, da fara aikin mayar da 'yan gudun hijiyar kasar Kongo Kinshasa dake zaune a kasashen waje zuwa yankunan su na ainihi.

Sannan masu ruwa da tsakin sun bayyana hakan ne a jiya Laraba, yayin wani taro da suka gudanar a birnin Kampala fadar mulkin kasar Uganda. Inda suka tattauna batutuwan da suka shafi yadda za a maida wadannan mutane zuwa kasar ta Kongo Kinshasa.

Har ila yau sun kuma sanar da cewa, za a yi kokarin lallashin mutanen da yawansu ya kai dubu 184 dake samun mafaka a Uganda a halin yanzu, domin su yarda da faran aikin mayar da su kasar ta su ta asali.

A nasu bangare Uganda da hukumar lura da 'yan gudun hijira ta MDD, za su gudanar da binciken jin ra'ayin jama'a tsakanin wadannan mutane, don mika wani rahoto ga Kongo Kinshasa a karshen watan Yuli mai zuwa. Kaza lika hukumar 'yan gudun hijirar ta alkawarta samar da motoci ga 'yan gudun hijirar dake da niyyar koma gidajen na su. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China