Dr Lomani a hirar sa da kamfanin dillanci labarai na kasar Sin Xinhua ya ce a da adadin wadanda suka mutu 13 ne sai daga baya aka samu Karin 18 abinda yasa ya zama 31.
Barkewar cutar Ebola dai ya fara ne a Djera wani dan kauye dake yankin arewa maso yammacin gundumar Equateur. (Fatimah Jibril)