in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabanin dake tsakanin Sin da Amurka ba za su hana hadin gwiwar kasashen biyu ba
2015-06-23 19:45:32 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yau yayin taron manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing cewa, bayan ci gaban da aka samu na kusan shekaru 30 har yanzu akwai makoma mai haske a dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasar Amurka, kuma sabanin dake tsakanin kasashen biyu ba zai hana hadin gwiwar dake tsakaninsu ba.

Bugu da kari, ya ce, a ganin Sin, babu shakka akwai bambancin ra'ayoyi har ma da 'yan sabani tsakanin kasashen biyu, amma ba su hana bunkasuwar dangantakar kasashen biyu ba, musamman ma a halin yanzu, ana ci gaba da habaka hadin gwiwar dake tsakaninsu, haka kuma, kasashen biyu suna iya cimma ra'ayi daya kan wasu batutuwa ta hanyar yin shawarwari, sa'an nan suna kuma kokarin inganta hadin gwiwar dake tsakaninsu domin cimma moriyar juna da kuma fuskantar kalubalolin da duniya ke fuskanta cikin hadin gwiwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China