in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi watsi da zargin Amurka na yi mata satar bayanai
2015-06-16 09:31:27 cri
Mahukuntan kasar Sin sun yi watsi da zargin da jami'an Amurka su yi mata na satar wasu muhimman bayanan soji da wasu manyan jami'anta.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Lu Kang ya shaidawa manema labarai cewa, babu kamshin gaskiya game da abin da Amurkan ke yayatawa.

Lu ya ce, duniya na sane da cewa, Amurka na satar bayanai ta fannoni dadan-danam kama daga siyasa, harkokin kasuwanci har ma da na daidaikun jama'a, kuma hakan ya sabawa dokokin kasa da kasa.

Don haka ya ja hankalin kasar ta Amurka da ta kwana da sanin cewa, akwai bukatar ta yi wa duniya bayani game da zargin da ake mata na satar bayanan jama'a, kafin ta zargi wasu da aikata irin wannan danyen aiki.

A farkon watan nan ne aka shiga rumbun adana muhimman bayanan ma'aikatan gwamnatin Amurka, inda santocin kasar da dama ke zargin Sin da aikatawa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China