in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ba ta da dalilin tsoma baki cikin ayyukan Sin a kudancin teku
2015-05-14 16:31:55 cri
Jakadan Sin dake kasar Amurka Cui Tiankai, ya shaidawa 'yan jarida na kafofin watsa labarun kasar Sin dake Amurka, cewa ayyukan da kasar Sin take gudanarwa a kudancin tekunta, ayyuka ne dake cikin hurumin mallakar yankunanta, kuma Amurka ba ta da dalili na tsoma baki cikin wadannan ayyuka.

Kaza lika jakadan ya ce Sin na fatan kasashen da wannan batu ya shafa, za su dauki matakan da suka dace wajen warware wannan matsala ta hanyar diplomasiyya.

Cui Tiankai ya yi nuni da cewa, Amurka ta dade tana yin baki biyu game zargin kasar Sin na gudanar da aikin shata yankunan kasa a kudancin tekunta.

Ya ce kasar Sin ba ta yi irin wannan aikin a wasu kasashe na daban ba, duk da cewa a baya wasu kasashen sun dauki irin wannan mataki a kan kasar ta Sin, kuma kasar Amurka ba ta taba zargin wadancan kasashen ba ko kadan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China