in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tashar wutar lantarki da ke yankin ciniki maras shinge na Lekki a Najeriya ta fara aiki
2015-05-27 20:37:20 cri
A jiya Talata ne, tashar samar da wutar lantarki dake yin amfani da gas mai karfin megawatt 12 ta fara aiki a yankin ciniki maras shinge na Lekki dake tarayyar Najeriya, kebabben yankin masana'antu daya tilo dake samar da wutar lantarki na tsawon sa'o'i 24 a ko wace rana a kasar Najeriya.

Kamfanin gina layin dogo na CRCC na kasar Sin ya shafe shakara daya wajen gina tashar, kuma gwamnan jihar Lagos Babatunda Fashola da zai bar gado a ran 29 ga watan da muke ciki ya halarci bikin kammala gina wannan tashar samar da wutar lantarki, inda ya latsa maballin tashar da kansa.

A sassa da dama na Najeriya ana amfani da na'urorin samar da wutar lantarki masu aiki da man dizal domin samar da wutar lantarki da makamashi, amma saboda karancin mai da ake fama da shi a 'yan shekarun nan, wasu na'urorin samar da wutar lantarki ba sa aiki yadda ya kamata, wannan ya sa a kan fama da karancin wutar lantarki a kullum. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China