in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da aikin gina tashar samar da wutar lantarki ta megawatt 100 a kasar Nijar
2013-04-05 10:16:36 cri
Shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou ya jagoranci a ranar Alhamis a kauyen Gorou Banda mai tazarar kilomita 10 daga birnin Niamey da bikin kaddamar da aikin gina tashar samar da wutar lantarki mai karfin megawatt 100.

Jimillar kudin wannan aiki ta tashi zuwa kusan Sefa biliyan 80 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 150, kuma wani kamfanin gine gine na kasar Sin na "Sino-Hydro" aka baiwa kwangilar gina wannan tasha da rabin kudaden suka fito daga kungiyoyin dake tallafawa kasar Nijar. Tashar za'a gina ta bisa fadin hekta 80 kuma aikin zai shafe tsawon watanni 20. A tsawon shekaru da dama, Niamey, babban birnin kasar Nijar da kuma sauran wasu kauyuka na kasar na fama da matsalar dauke wutar lantarki ta tsawon sa'o'i a cikin yini musamman a lokacin tsananin zafi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China