in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ECOWAS ta kebe dala miliyan 107 domin samar da wutar lantarki a kasashe 3
2013-12-17 14:33:48 cri

An cimma wata yarjejeniyar zuba jari ta gamayyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS domin samar da kudade ga kasashe 3 wato Gambiya, Sierra Leone da Mali a bangaren samar da wutar lantarki bisa jimillar dalar Amurka miliyan 107.94 a ranar Litinin a birnin Abidjan na kasar Cote d'Ivoire.

An sanya hannu kan wannan yarjejeniya a gabanin taron kwamitin ministocin ECOWAS karo na 71 dake cikin tsarin gaggauta samar da makamashin wutar lantarki.

Kasashen uku za su samu wadannan kudade, inda kasar Gambiya za ta samu dalar Amurka miliyan 31.8, kasar Mali dalar Amurka miliyan 54.34, ita kuma kasar Sierra Leone za ta samu dalar Amurka miliyan 21.8.

Shirin na musamman da za'a aiwatar tare da tallafin kudin kungiyar ECOWAS, za'a yi shi bisa matakin taimakon kai tsaye ga wadannan kasashe uku inda ayyukan samar da wutar lantarki suke kasa ga bukatun jama'a, kuma yawan hanyoyin samun bunkasuwar tattalin arzikin sun kasance kalilan a manyan biranen wadannan kasashe uku da suka hada da Banjul, Bamako da kuma Freetown. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China