in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron shugabannin kungiyar AL na mai da hankali kan yanayin tsaron yankin
2015-03-29 16:32:46 cri
Jiya Asabar 28 ga wata, an bude taron shugabannin kungiyar tarayyar kasashen Larabawa wato AL karo na 26 a birnin Sharm el Sheikh, inda mahalarta taron suka mai da hankali sosai kan yadda za a iya fuskantar matsalar tsaro a yankin nasu.

Shekarar bana shekara ce ta cika shekaru 70 na kafuwar kungiyar AL, kuma babban taken taron shugabannin kungiyar na wannan karo shi ne "shekaru 70 na kungiyar AL, a kiyaye tsaron kasashen".

Bugu da kari, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya halarci bikin bude taron, inda ya ba da jawabi cewa, rikice-rikice, yake-yake da kuma hare-haren ta'addanci na ci gaba da kasancewa a nan duniya, wadanda ba kawai suna kawo barazana ga tsaron yankin Larabawa, har ma kuma suna kasancewa babban kalubale ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa. Dalilin haka ne, Ban Ki-moon ya yi kira ga kungiyar AL da ta yi hadin gwiwa tare da gamayyar kasa da kasa, domin neman hanyar siyasa wajen warware wadannan matsaloli. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China