in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AL ta jaddada ra'ayinta na zargin wasu kasashe da tsoma baki cikin harkokin kasar Libya
2015-01-06 14:16:38 cri
Kungiyar tarayyar kasashen Larabawa wato AL, ta gudanar da wani taron gaggawa a jiya Litinin, domin tattaunawa game da halin da ake ciki a kasar Libya.

Bayan taron, majalisar kungiyar ta AL ta fidda wata sanarwa, inda ta nuna damuwa matuka game da tsanantar halin nuna karfin tuwo da ake ciki a kasar Libya. Kungiyar ta kuma jaddada cewa, tilas ne a girmama ikon mulkin kai, da 'yancin kai, da dinkewar kasar baki daya, da ma cikakken yankin kasar Libya, da bijirewa tsoma bakin kasashen waje ckan harkokin cikin gidan kasar.

Sanarwar ta bayyana cewa, wakilan kasashe mahalarta taron na ganin hanya daya tilo da ta dace a bi, domin warware matsalar Libya ita ce hanyar siyasa, bisa tushen cimma daidaito tsakanin kungiyoyin kasar daban daban. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China