in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Beji Caid Essebsi ya ci zaben zama kasar Tunisiya
2014-12-30 11:09:43 cri

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar Tunisiya, a yammacin ranar 29, ta sanar da sakamakon zabe dake bayyana mista Beji Caid Essebsi a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar Tunisiya.

A cewar hukumar zaben Tunisiya, mista Beji Caid Essebsi ya lashe zaben da kashi 55.68 cikin 100 na kuri'un da aka jefa, yayin da abokin takaransa Moncef Marzouki shugaba mai barin gado ya samu kashi 44.32 cikin 100 na kuri'un da ake jefa.

Beji Caid Essebsi mai shekaru 88 a duniya zai yi rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasar Tunisiya a ran 31 ga wata, wanda kuma zai kasance shugaban kasar Tunisiya na biyar, kana shugaba na farko da jama'ar kasar suka zaba bayan juyin juya halin da aka yi a kasar a shekarar 2011. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China