in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kada kuri'u a babban zaben kasar Tunisiya
2014-12-21 20:57:59 cri
Da sanyin safiyar Lahadin nan ne al'ummar kasar Tunisiya suka fara kada kuri'u, a zagaye na biyu na babban zaben kasar, zaben da ake fatan wanda ya lashe shi, zai kasance sabon shugaban kasar a karon farko cikin shekaru 4, tun bayan boren da ya janyo hambarar da gwamnatin Zine Abedine Ben Ali, da kuma tashe tashen hankulan da suka biyo baya a karshen shekarar 2010 da kuma farkon shekarar 2011.

Sama da al'ummar kasar miliyan 5 da dubu dari 3 ne dai ake sa ran zasu kada kuri'un su, domin zabar ko dai Beji Caid Essebsi mai ra'ayin 'yan ba ruwan mu daga jam'iyyar Nidaa Tounes, ko kuma shugaban kasar na yanzu Moncef Marzouki na jam'iyyar masu ra'ayin Islama ta Ennahda.

A zagayen farko na zaben Mr. Essebsi ne ya lashe mafiya yawancin kuri'un da aka kada, da kason 39.46 bisa dari, ya yin da Marzouki ke biye da kaso 33.43 bisa dari.

Tuni dai 'yan kasar dake kasashen waje suka fara kada na su kuri'u tun a ranar Alhamis, za kuma a ci gada da zaben har zuwa wayewar garin Litinin. Hukumar zaben kasar ta ce za ta sanar da sakamakon fari, na wannan zagayen zabe a goben.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China