in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Afirka na hadin gwiwa wajen kiyaye kayayyakin tarihi a fannin al'adu da aka gada daga kaka da kakanni
2014-09-24 20:37:29 cri
Wasu jami'an kula da harkokin al'adu da masana daga kasashen Afirka guda 18 sun halarci dandalin tattaunawar kiyaye kayayyakin tarihi a fannin al'adu da aka gada daga kaka da kakanni na Sin da Afirka da aka gudanar a birnin Beijing a ran 23 da 24 ga wata, inda suka tattauna tare da masanan al'adu na kasar Sin kan manufofin kiyaye kayayyakin tarihi a fannin al'adu, fasahohin da abin ya shafa da kuma yadda za a iya karfafa hadin gwiwar Sin da Afirka kan wannan fanni da dai sauransu.

A cikin jawabinsa, mataimakin ministan harkokin al'adu na kasar Sin Ding Wei ya jaddada muhimmancin kiyaye kayayyakin tarihi a fannin al'adu da aka gada daga kaka da kakanni wajen ba da gudumawa ga ci gaban al'adun ko wace kasa da kuma al'adun kasashen duniya, bugu da kari, ya kuma bayyana bukata da kuma fatansa dangane da hadin gwiwar Sin da Afirka kan kiyaye kayayyakin tarihi a fannin al'adu da musayar ra'ayoyi a tsakaninsu kan wannan fannin.

A nasa bangaren, ministan harkokin al'adu na kasar Zimbabwe Andrew Langa ya yi bayani kan tahiri da kuma halin da kasar ke ciki a aikin kiyaye kayayyakin tarihi na al'adu, ya kuma bayyana ra'ayoyinsa kan yadda za a iya ciyar da hadin gwiwar Sin da Afirka kan wannan aikin gaba, kara wa juna sani kan aikin da kuma yadda za a iya habaka harkokin al'adun Sin da Afirka a nan gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China