in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta kara yayata karfin da take da shi na al'adu
2014-01-01 16:47:11 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya lashi takwabin kara yayata al'adun kasar, ta hanyar yayata al'adun Sinawa na zamani tare da nuna tarin al'adun da Allah ya hore wa Sinawa ga sauran kasashen duniya.

Shugaba Xi ya bayyana hakan ne ranar Litinin yayin jawabin da ya gabatar a wani taron mambobin hukumar kula harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na JKS

Ya kuma yi kiran da a kara kokarin yayata al'adun kasar mai tsarin gurguzu, zurfafa yin gyare-gyare a tsarin al'adu, da karfafa tunanin kirkire-kirkiren al'adu na jama'a, matakan da ya yi imanin cewa, za su daga matsayin kasar Sin a bangaren al'adu a idon duniya.

Shugaban ya ce, kamata ya yi a yayata labarun da suka shafi kasar Sin, da manufofinta, ta haka duniya za ta kara fahimtar tsare-tsaren kasar Sin na musamman.

Don haka, ya ce, kamata ya yi a yi amfani da hanyoyin sadarwa na zamani yadda ya kamata, da kara yin kirkire-kirkire, ta yadda kwalliya za ta biya kudin sabula ta wannan fuska.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China