in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar nuna kayayyakin fasahar hannu ta Nanjing ta kasar Sin ta kai ziyara a tarayyar Najeriya
2014-07-25 14:54:13 cri
A ranar 24 ga wata da yamma ne, tawagar nuna kayayyakin fasahar hannu ta birnin Nanjing da ke kasar Sin ta nuna wa al'ummar tarayyar Najeriya fasahar hannu daga kasar Sin a cibiyar al'adu ta kasar Sin dake birnin Abuja. Inda masu fasaha na kasar Sin suka yi mu'amala tare da 'yan kallo na Najeriya, tare da ba su kyaututukan kayayyakin fasahar hannu, wadanda suka samu karbuwa sosai.

Tawagar ta je Najeriya ne don halartar bikin baje koli karo na 6 na kayayyakin fasaha na nahiyar Afirka da ake shiryawa a Abuja.

A yayin bikin, mai ba da shawara a kan harkokin al'adu na ofishin jakadancin Sin dake tarayyar Najeriya Yan Xiangdong ya bayyana cewa, fasahar hannu wata nau'in fasaha ce ta jama'a, hakan ya sa ya samu amincewa daga jama'a cikin sauki. Masu fasaha daga birnin Nanjing na kasar Sin sun nuna wa al'ummar Najeriya fasahohinsu, ana sa rai wannan matakin zai taimaka wajen cudanyar al'adu a tsakanin kasashen biyu.

Bugu da kari, Mr. Yan ya nuna fatansa na ganin masu fasaha na kasar Sin za su kara komawa kasar ta Najeriya tare da halartar bukukuwan al'adu, ta yadda jama'ar kasar za su samu damar ganin kayayyakin fasaha masu dimbin yawa dake dacewa da rayuwarsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China