Hukumar ta kuma bayyana cewa, ya zuwa yanzu, an fi samu rasuwar rayuka a kasar Guinea, yayin da kasar Saliyo ta kasance kasar da aka fi samun mutanen da suka kamu da cutar.
A wannan rana, manyan jami'an hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, wasu jami'an kasashen dake fama da cutar da kuma wasu masanan kiwon lafiya na kasa da kasa sun halarci taron na gaggawa da WHO ta kira a asirce.
Za a kashe kwanaki biyu ana gudanar da taron, sai dai ba za a gabatar da sakamakon taron ba har sai a ranar 8 ga wata.
Kana bisa labarin da hukumar WHO ta samar, an ce, idan har taron ya tabbatar cewa, cutar Ebola da ake ciki a halin yanzu ta kasance lamarin kiwon lafiyar jama'a ta gaggawa dake janyo hankulan kasa da kasa, to za a gabatar wa babbar sakatariyar WHO Margaret Chan Fung Fu-chun matakan gaggawa da za a dauka kan wannan cuta. (Maryam)