in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Likitan da ya duba lafiyar wanda ya kamu da cutar Ebola, shi ma cutar ta kama shi, a cewar gwamnatin Nijeriya
2014-08-05 10:46:41 cri

Ministan lafiya na kasar Nigeria Onyebuchi Chukwu ya ce, likitan da ya duba lafiyar wani dan kasar Liberia mai dauke da cutar Ebola a birnin Legas, shi ma a halin da ake ciki cutar ta kama shi.

Ministan ya ce, a halin da ake ciki ana binciken lafiyar wani likita na daban, wanda shi ma ya duba lafiyar mai dauke da cutar domin a gano ko shi ma cutar ta kama shi.

Likitocin guda biyu sun duba lafiyar Patrick Sawyer, wani dan kasar Liberia, wanda a karshe ya mutu a Nigeria, kusan makonni biyu da suka wuce, a sakamakon kamuwa da cutar Ebola.

Ministan lafiyar na Nigeriar ya ce, an baiwa jiragen kasashen waje umurni, da kar su sake shigo Nigeria da gawarwakin mutanen da suka mutu a sakamakon cutar Ebola daga wasu kasashe.

Hukumomin na Nigeria dai sun ce, ba za su rufe kan iyakarsu ba a sakamakon cutar Ebola, wacce ba ta da magani, sai dai idan yin hakan ya zama dole. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China