in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba ta yarda da zargin hana 'yancin addini da Amurka ta yi mata
2014-07-30 20:15:45 cri
A jiya Talata 29 ga wata ne, majalisar gudanarwa ta kasar Amurka ta fitar da rahoron bincike kan 'yancin addini na kasa da kasa na shekarar 2013, inda ta ci gaba da mai da kasar Sin a matsayin kasa ta musamman da ya kamata a mai da hankali kan yanayin da take ciki.

Dangane da haka, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya bayyana a yau Laraba 30 ga wata cewa, gwamnatin kasar Sin na kiyaye 'yancin bin addini na jama'ar kasar bisa dokoki yadda ya kamata, kuma dukkanin jama'ar kasar suna da 'yancin addini bisa dokokin kasar. Kasar Sin ba za ta yarda da zargin da kasar Amurka ta yi mata ba game da wannan batu.

Sin ta kuma nuna bacin rai dangane da zargin da bai dace ba da Amurka ta yi kan manufofin addini na kasar Sin. Don haka ta yi kira ga kasar Amurka da ta kawar da bambancin ra'ayin siyasar da take nunawa kasar Sin, ta kuma daina tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasar Sin ta hanyar yin amfani da batun addini. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China