in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Cote d'Ivoire ya yi kira ga jama'arsa da su bi matakan rigakafin cutar Ebola da gwamnatin ke dauka
2014-07-15 14:22:18 cri
A ranar litinin 14 ga wata, shugaban kasar Cote d'Ivoire Alassane Ouattara ya yi kira ga jama'ar kasar da su bi matakan rigakafin cutar Ebola da gwamnatin kasar take dauka don kare bullar cutar a kasar.

A kwanakin baya, don magance yiwuwar samun cutar Ebola a kasar Cote d'Ivoire, ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar ta bada umurnin kara daukar matakan sa ido kan cutar, da hana jama'ar kasar su ci namun daji, da kara sa ido kan mutane dake zirga-zirga a yankin iyakar kasa a tsakaninta da kasashen Guinea, Liberia da Saliyo wadanda aka samu cutar Ebola a cikinsu. Ya zuwa yanzu, ba a gano ko wane mutum da ya kamu da cutar Ebola a kasar ta Cote d' Ivoire ba.

Bisa kididdigar da hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO ta yi, an ce, ya zuwa ranar 8 ga watan Yuli, mutane 888 a kasashen Guinea, Liberia da Saliyo sun kamu da cutar Ebola ko ake zargin su da kamuwa da shi, guda 539 a cikinsu sun rasa rayukansu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China