in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Cutar Ebola dake yaduwa a yammacin Afirka ta haddasa mutuwar mutane kimanin 470
2014-07-02 14:48:17 cri
Cutar Ebola da ta bulla da farko a kasar Guinea a watan Febrairu ta ci gaba da yaduwa a yammacin Afirka a wadannan watanni. Bisa kididdigar da hukumar kiwon lafiya ta duniya ta yi, an ce, mutane 759 sun kamu da cutar, kuma 467 daga cikinsu sun mutu.

Bisa kididdigar, kasar Guinea ta fi sauran kasashe yawan masu cutar ta Ebola, inda mutane 413 suka kamu da ita, cikinsu 303 sun rasa rayukansu. A kasar Liberia, akwai mutane 107 da suka kamu da cutar, kuma 65 a cikinsu sun mutu. Sai kuma kasar Saliyo, inda mutane 99 a cikin masu fama da cutar 239 suka mutu. An ce, yawan mutane da suka kamu da cutar da wadanda suka mutu a sakamakon kamu da cutar ya kai matsayin koli a tarihi.

Don hana yaduwar cutar ta Ebola, ministocin kiwon lafiya na kasashen yammacin Afirka 11 za su gudanar da wani taron gaggawa a Accra dake kasar Ghana a ranakun 2 da 3 ga watan nan, inda za su tsara shirin hadin gwiwar kasa da kasa wajen tinkarar cutar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China