in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya tsawaita wa'adin aikin tawagar kasar Cote d'Ivoire
2014-06-26 14:35:06 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya zartas da wani kuduri na tsawaita aikin tawagar wanzar da zaman lafiya ta musamman dake kasar Cote d'Ivoire har tsawon shekara daya.

Kwamitin sulhu na MDDr wanda ya gudanar da wani taro kan halin da kasar ta Cote d'Ivoire ke ciki a jiya Laraba, inda ya zartas da wannan kuduri da zai kara wa'adin aikin tawagar zuwa ranar 30 ga watan Yunin shekarar 2015.

Ana dai fatan wannan tawaga za ta bada gudummawa ga mahukuntan kasar Cote d'Ivoiren wajen shirya zaben shugaban kasar da ke tafe cikin shekarar ta 2015. Baya ga taimakawa bangarori daban daban na masu ruwa da tsaki a fagen shafar siyasar kasar wajen gudanar da shawarwari. Koda yake dai batun tabbatar da tsaron rayukan fararen hula shi ne aiki mafi muhimmanci ga tawagar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China