in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Cote d'Ivoire ya yaba da goyon bayan da kasar Sin ke baiwa kasarsa
2014-01-04 17:01:14 cri
A Jiya Jumma'a 3 ga wata ne, Firaministan kasar Cote d'Ivoire Daniel Kablan Duncan ya nuna yabo sosai ga goyon bayan da kasar Sin ta baiwa kasarsa dangane da samar da manufofin ba da gatanci ga kasar don taimako mata wajen sake gina kasar.

Yayin da yake amsa tambayoyin da manema labaran kasar Faransa suka yi masa a birnin Abidjan na kasar Cote d'Ivoire, Mr.Duncan ya bayyana cewa, kasar Sin ta samar da manufofin ba da gatanci da dama ga kasar Cote d'Ivoire kan ayyukan hadin gwiwar tattalin arzikin dake tsakanin kasashen biyu. Ya ce, gwamnatin kasar Sin da wasu bankunan kasar Sin sun samar da taimakon kudi da manufofin ba da gatancin rancen kudi ga kasar Cote d'Ivoire don samar da kayayyakin more rayuwa ga la'ummar kasar.

Ya kuma kara da cewa, bai kamata kawai kassahen yammacin su zargi masu zuba jari na kasar Sin dangane da samun albarkatun ma'adinai a nahiyar Afirkaba, ya ce, Sinawa sun taimaka mana wajen raya kasarmu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China