in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Cutar Ebola a yammacin Afirka na karkashin kulawa, in ji wani jami'in WHO
2014-07-11 16:51:39 cri
A Jiya Alhamis 10 ga wata, a birnin Konakry, hedkwatar kasar Guinea, mataimakin babban sakataren kungiyar kiwon lafiya ta duniya (WHO) dake mai kulawa da batun tsaron kiwon lafiya na kungiyar kiwon lafiya ta duniya (WHO), mista Keiji Fukuda ya bayyana cewa, a yanzu ana kulawa da cutar Ebola a yammacin Afirka yadda ya kamata.

Yayin da yake magana da 'yan jarida, Keiji Fukuda ya bayyana cewa, yanzu cutar Ebola dake yaduwa a kasashen Guinea da Liberia da kuma Sierra LeoneSaliyo na ci gaba da yaduwa, amma ana iya kulawa da ita, Sannan sannan kuma ana cikin wani yanayi mai kyau na yin rigakafi da kuma yaki da ita. A sa'i daya kuma, ya yaba a kan jerin matakan da gwamnatin Guinea ta dauka bayan barkewar cutar Ebola, wato kara sa ido, ba da jiyya da kebe wadanda suka kamu da cutar zuwa wuri na daban, da kafa dakin gwaji, da kara karfin fadakarwa da sauransu.

Feiji Fukuda ya je birnin Konakry ne bayan da ya halarci taron gaggawa na ministocin kasashen yammacin Afirka da aka shirya a birnin Accra, hedkwatar Ghana a ranar 2 ga wata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China