in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya taya Afghanistan murnar kada kuri'u a babban zaben shugaban kasa zagaye na biyu
2014-06-15 16:25:23 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya taya kasar Afghanistan murnar sake kada kuri'u a babban zaben kasar zagaye na biyu, da ya gudana ranar Asabar cikin kyakkawan yanayi.

Cikin wata sanarwa da aka fitar, Mr. Ban ya jinjinawa kwazon al'ummar kasar ta Afghanistan, wadan da ya ce sun kada kuri'u cikin himma, lamarin da ke nuna aniyarsu ta gina makoman kasarsu yadda ya kamata, da kuma kawar da tashe-tashen hankula.

Mr. Ban ya kuma jaddada cewa, ya zama wajibi ga hukumar dake lura da babban zaben kasar, ta kidaya kuri'un da aka kada yayin zaben bisa adalci kuma ba tare da wani jinkiri ba.

Kaza lika, Mr. Ban ya bukaci 'yan takarar babban zaben kasar da magoya bayansu, da su mutunta, tare da baiwa hukuma mai lura da zaben goyon bayan da ya wajaba. Ya ce, cikin 'yan makwanni masu zuwa, ana fatan wanzuwar yanayin hadin gwiwa da farin ciki tsakanin al'ummun kasar, game da babban zaben da ya gabata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China