in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban babban taron MDD ya yi kira da a shigar da mata, matasa da zaman takewar al'umma cikin ajandar bunkasuwa bisa fannoni daban daban bayan shekarar 2015
2014-03-07 16:18:44 cri
A jiya Laraba 6 ga wata ne, babban taron MDD karo na 68 ya kira taro na kwanaki biyu, mai taken babbar gudumawa da mata, matasa, zaman takewar al'umma za su bayar ga ajandar bunkasuwar kasa da kasa bayan shekarar 2015, don murnar ranar mata ta kasa da kasa wato 8 ga watan Maris.

Yayin bikin bude taron, shugaban babban taron MDD karo na 68 John W. Ashe ya yi jawabin cewa, babban taken ranar mata ta kasa da kasa na shekarar bana shi ne, adalcin mata shi ne bunkasuwar dan Adam, in dai ba a iya kiyaye hakkin mata da yawansu ya kai rabin al'ummar duniya tare da girmama ilminsu da kuma kwarewarsu ba, ba za a iya raya al'adu da fasahohin bil Adam yadda ya kamata ba.

Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Wang Min ya bayyana a yayin taron cewa, tabbatar da zaman daidai wa daida tsakanini maza da mata da kuma kare 'yancin mata, su ne manyan ayyukan da za su iya nuna bunkasuwar zaman takewar al'umma da kuma ci gaban kasa da kasa. Kasar Sin tana goyon bayan da a mai da hankali kan batun mata, musamman ma kan fannonin bunkasuwar tattalin arzikin mata da kuma saukaka fatara da sauran fannoni. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China