in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manyan wakilan jama'a da masu bada shawara game da siyasa na kasar Sin sun bukaci kwakkwaran mataki akan 'yan ta'adda bayan harin Kunming
2014-03-02 17:21:08 cri
Manyan wakilan jama'a da masu ba da shawarar game da siyasa sun bayyana goyon bayan su a kan daukan kwakkwaran mataki ma 'ta'addanci sakamakon wani hari na kan mai uwa da wabi da wassu masu neman ganin ballewar jihar xinjiang suka aikata wanda ya hallaka mutane 29 a yammacin ranar asabar 1 ga wata.

Babban Jami'i na na kwamitin kwararru na sojojin kasar Sin bangaren sojin ruwa,Yin Zhuo a cikin bayanin sa,yace ya kamata a kaddamar da gangamin wayar da kan jama'a akan ayyukan 'yan ta'adda a kuma hadu gaba daya a yake su.

Yin wanda har ila yau mamba ne na kwamitin ba da shawara kan harkokin siyasar kasar yace wannan shirin na 'yan ta'adda da aka yi shi a tsanake ba ya da alaka da addini ko kabilanci, magana ce kawai ta ta'addanci dake da alaka da kungiyoyin ta'addancin na kasashen waje.

Kalamansa ya biyo bayan wani hari da wukake ne da 'yan neman balle jihar xinjiang suka kai ga al'umma a tashar jirgin kasa a Kunming dake kudu maso yammacin kasar Sin. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China