in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi Allah wadai da harin ta'addancin da aka kai birnin Kunming
2014-03-02 10:49:32 cri
Babban magatakardan MDD mista Ban Ki-moon ya sa mai magana da yawunsa ya fitar da wata sanarwa a ranar Asabar 1 ga wata, inda ya nuna takaicinsa matuka kan abkuwar harin ta'addanci a birnin Kunming dake kudancin kasar Sin, tare da bayyana fatansa na ganin an gurfanar da masu aikata harin gaban kotu.

Cikin sanarwarsa, mista Ban ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu sakamakon harin, gami da nuna fatan alheri ga wadanda suka ji rauni don su samu sauki cikin sauri. Mista Ban ya jaddada cewa, kashe-kashen da aka yi ma jama'ar wadanda ba su san hawa ba ba su san sauka ba ba zai samu wata hujjar da za ta zauna da gindinta ba.

A daren Asabar 1 ga wata misali karfe 9 da minti 21 bisa agogon kasar Sin, wasu mutanen da suka rufe fuskokinsu sun yi amfani da wuka wajen kai hari ga jama'ar da suke tashar jirgin kasa na birnin Kunming, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 29, da jikkatar wasu fiye da 130 zuwa lokacin da aka watsa wannan labari. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China