in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata kotu a Afrika ta kudu ta amince da watsa shari'ar da za a yiwa Oscar Pistorius kai tsaye ta Talabijin
2014-02-26 16:54:44 cri
Wata kotu a Afrka ta kudu ta yanke shawarar cewa, ta ba da izni ga gidan telibijin kasar da ya watsa zaman shari'ar da za a yiwa Oscar Pistorius kai tsaye.

Oscar Pistorius mai shekaru 27 a duniya, kana shahararen dan tseren nakasassa. Ana tuhumarsa da laifin kashe budurwarsa,inda za a yanke masa hukunci a ran 3 ga watan Maris.

Babbar kotun kasar ta yanke shawara a jiya Talata 25 ga wata cewa, ta yarda da rokon da wasu kafofin yada labarai suka yi na neman a watsa shari'ar da za a yi masa kai tsaye ta Talabijin, amma ba ta yarda a dauki hoton bidiyon Oscar Pistorius da masu kare shi ba da sauransu,yayin da su kuma gidajen rediyo aka amince musu su watsa sautin zaman kotun.

Kafofin yada labarun kasar na ganin cewa, watsa shari'ar kai tsaye ta kafofin wtasa labarai zai taimaka wajen yanke hukunci cikin adalci. Amma lauya dake kare Oscar ya ce, wannan mataki katsalandan shari'a ne ga wanda ake tuhuma.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China