in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu ta aiwatar da sabuwar manufar yaki da cin hanci da rashawa
2013-02-25 17:22:36 cri
A Lahadi 24 ga wata, minista mai kula da harkokin dokokin kasar Afrika ta Kudu Jeff Radebe, ya bayyana cewa, gwamnatin kasar za ta aiwatar da sabuwar manufar yaki da cin hanci da rashawa, ciki har da bayyana sunayen masu laifi da gabatar da labaru filla-filla game da yadda suka aikata ci hanci da rashawa, tare da hana su gudanar da aiki bisa matsayinsu.

Ministan ya fada wa manema labaru cewa, za a gabatar da labarunsu ta hanyar mujallu da jaridu da gidajen rediyo na kasar.

Haka kuma, an ce, wannan manufar da aka fitar na da ma'anar musamman, wajen ba da tabbaci wajen yaki da cin hanci da rashawa.

A cikin kwanaki masu zuwa, za a fidda da dukkan sunayen wadanda da aka tabbatar da laifin cin hanci da rashawa, kuma za a rufe asusun ajiyarsu, ko kuma a mayar da asusun ga gwamnati.

Haka kuma, ministan ya waiwayi baya game da kokarin da ya yi wajen yaki da cin hanci da rashawa, tun bayan da aka kafa sashen kula da yaki da cin hanci da rashawa a kasar a shekarar 2010.

Bisa kididdigar da Radebe ya bayar, an ce, an cafke mutane 237, tare da yin hukunci ga 32 daga cikinsu, haka kuma an wanke 2 daga cikin zargin da aka yi musu, sauran 203, sun fuskantar shari'a a halin da ake ciki.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China