in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya halarci taron koli karo na 8 na gabashin Asiya
2013-10-11 15:20:50 cri
Firaministan kasar Sin Mr Li Keqiang, ya halarci taron koli karo na 8 na kasashen gabashin Asiya a birnin Bandar Seri Begawan, na kasar Brunei. Shugabanni ko wakilan kasashe 10 na kungiyar tarayyar kasashen yankin kudu maso gabashin Asiya (ASEAN) da na kasashen Korea ta kudu, da Japan, da Amurka, da Rasha, Indiya, da Austriliya, da New Zealand da dai sauransu sun halarci taron.

A cikin jawabinsa, Le Keqiang ya ba da shawarar kara hadin gwiwa wajen tinkarar kalubaloli tare. Ya kuma bayyana bukatar sanya kulawa ga manufar bunkasa, da ta hada da batun ingancin hatsi da na makamashi, da kariya daga bala'u daga Indallahi, da batun sauyin yanayi, kiwon lafiya da sauran muhimman batutuwa.

Ban da haka, Le Keqiang ya ba da shawarar kafa wani tsarin tsaro da zai dace da halin da ake ciki a wannan yanki, tare da biyan bukatun da ake yi daga fannoni daban-daban.

Haka zalika, Li Keqiang ya bayyana matsayin kasar Sin kan batun tekun Kudu, yana mai cewa, Sin za ta yi kokari tare da kasahen ASEAN, wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin tekun Kudu, da aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla a baya, tare da kaddamar da ka'idar tekun bisa matsayar da suka cimma.

A hannu guda kuma, shugabannin kasashen ASEAN na fatan daidaita batun tekun Kudu cikin lumana, tare kuma da yin hadin kai wajen tabbatar da zaman lafiya da karko, da ma wadatar yankin. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China