in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Masar ya yi kira da a kakkabe makaman nukiliya daga gabas ta tsakiya
2013-09-29 21:00:30 cri
Ministan harkokin wajen kasar Masar Nabil Fahmy, ya furta a ran 28 ga wata a hedkwatar MDD dake birnin New York cewa, yana fatan kasashen duniya za su dauki matakin da ya dace, don mai da yankin gabas ta tsakiya maras makaman nukiliya.

Yanzu haka an shiga rana ta biyar da yin babbar muhawarar taron MDD karo na 68, a cikin jawabinsa, Nabil Fahmy ya nuna cewa, ba za a iya samar da wani sabon yanayi a gabas ta tsakiya ba, muddin ba a kawar da makaman nukiliya, da makaman kare-dangi ba, kuma rashin daukar wannan mataki a cewarsa na iya kawo nakasu ga yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya.

Bugu da kari Fahmy ya kalubalanci kasar Isra'ila, da ta shiga yarjejeniyar hana yaduwar marasa makaman nukiliya. Ya ce ya kamata kasashen duniya sun yi kokarin gudanar da taron kawar da makaman nukiliya a yankin gabas ta tsakiya, a karshen wannan shekara ko a farkon shekara mai zuwa, wanda a baya aka jinkirta gudanar da shi a shekara da ta gabata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China