in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
EU ta aikawa shugaban kasar Kenya wasika domin neman hadin kai wajen yaki da ta'addanci
2013-09-24 15:00:10 cri

Shugaban majalisar gudanarwa ta kungiyar tarayyar kasashen Turai ta EU Von Rompuy da shugaban majalisar mambobin EU Manuel Durao Barroso sun aikawa shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta wata wasika a jiya Litinin 23 ga wata, inda suka bayyana fatan yin hadin kai da kasar Kenya domin yaki da ta'addanci, da kuma murkushe kungiyar masu tsattauran ra'ayin Islama ta kungiyar matasan Somaliya ta SYP, domin shimfida zaman lafiya da karko a kasar Somaliya, ta yadda 'yan gudun hijira za su koma kasarsu da sauri.

Ban da haka, shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mohamud ya nuna a wannan rana cewa, akwai alamar yaduwar SYP a duniya, ba ma kawai abin zai kawo babbar illa ga nahiyar Afrika ba har ma ga dukkan duniya don haka gwamnatin kasar Somaliya tana dukufa kan murkushe SYP bisa karfinta yadda ya kamata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China