in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fadar shugaban kasar Afirka ta Kudu ta ce Mandela na ci gaba da murmurewa
2013-07-23 14:46:24 cri
Wasu rahotanni daga fadar gwamnatin Afirka ta Kudu na cewa tsohon shugaban kasar Nelson Mandela na murmurewa sannu a hankali, ko da yake dai yanayin rashin lafiyar da yake fama da shi na da tsanani.

Mai magana da yawun fadar shugaban kasar Mac Maharaj ne ya bayyana hakan cikin wata sanararwa da ya fitar a ranar Litinin, biyowa bayan ziyarar da shugaban kasar Jacob Zuma ya kaiwa Mr. Mandela a asibitin da yake kwance.

Da yake tsokaci ga manema labarai bayan ziyarar da ya kai ga tsohon shugaban, Zuma ya yi kira ga masoya da masu fatan alheri ga Mandela, da su ci gaba da gudanar da addu'o'i kamar yadda suka saba.

Yanzu dai kwanaki 44 ke nan da kwantar da Mandela a asibiti, kuma wannan sanarwa ita ce ta farko tun bayan wadda aka fitar ranar bikin cikarsa shekaru 95 da haihuwa, wadda ke kunshe da ra'ayin fadar gwamnatin kasar dangane da halin da yake ciki.

Bugu da kari shima wani jika ga tsohon shugaban kasar mai suna Mandla, ya bayyana yadda Mandelan ke dada samun sauki, yana mai cewa hakan wani lamari ne mai matukar karfafa gwiwa.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China