in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mandela ya kai rana ta biyar a asibiti
2013-04-02 10:01:18 cri
Ofishin shugaban kasar Afirka ta kudu ta bayyana cewa zuwa ranar Litinin, tsohon shugaban kasar Nelson Mandela ya shafe kwanaki biyar kwance a asibiti kuma har yanzu ba'a samu wani muhimman ci gaba ba dangane da yanayin lafiyar jikin nasa.

Mai magana da yawun fadar shugaban kasar Mac Maharaj ya bayyana cewa ana yi wa Mandela jiyyar cutar sanyi ta pneumonia kuma har yanzu babu wani canji a jikin nasa tun bayan bayani da aka bayar ranar Lahadi.

Ya ci gaba da cewa, iyalansa sun kasance tare da shi a wannan rana kuma suna nuna godiya dangane da irin goyon baya da jama'a ke ba su.

Mandela wanda yanzu shekarunsa na haihuwa sun kai 94, an sake kwantar da shi a asbiti ne ranar 28 ga watan Maris saboda cutar hakarkari da ta sake taso masa.

Wannan shi ne karo na biyu da aka kwantar da Mandela a cikin wata guda. Ranar 9 ga watan Maris an kwantar da Mandela a wani asibiti a birnin Pretoria don binciken lafiyarsa a matsayin matakin lura da yanayin jikinsa saboda shekarunsa. Kashegarin wannan rana aka sallame shi. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China