in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Zuma na Afirka ta Kudu ya yi kira da a karrama gudummawar da Mandela ya bayar
2013-07-18 10:32:53 cri
Gabanin kankamar bukukuwan ranar tunawa da tsohon shugaban kasar Afirka ta Kudu Nelson Mandela, musamman kan gudummawar da ya bayar ta fuskar yaki da akidar nuna wariyar launin fata, shugaba Jacob Zuma na Afirka ta Kudu, yace babu wata hanya mafi dacewa ta girmamawa wannan gudummawa da Mandela ya bayar, wadda ta wuce aiki tukuru wajen ginin magartacciyar al'umma.

Shugaba Zuma ya yi wannan jawabi ne a ranar Laraba 17 ga wata, ta bakin kakakinsa Mac Maharaj, inda ya taya daukacin al'ummar kasar murnar zagayowar wannan rana ta kasa da kasa da ake kebe, domin tunawa da irin gudummawar da Mandela ya baiwa rayuwar al'umma, tare da fatan cimma dukkanin kyawawan burikan da aka sanya a gaba, gabanin mintina 67 da za a shafe ana gudanar da ayyukan tallafawa rayuwar al'umma a ranar Alhamis.

Mandela wanda zai cika shekaru 95 a bana, zai yi bikin ranar haihuwarsa na wannan shekara ne a gadon asibiti, sakamakon wata cutar huhu da yake fama da ita tsahon lokaci. (Saminu Alhassan Usman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China