in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha na kin amincewa da tsoma baki cikin harkokin kasar Sham ta hanyar daukar matakin soja
2013-04-18 15:32:45 cri
Babban sakataren MDD Mr Ban Ki-Moon ya yi nuni a ran 17 ga wata cewa, halin da ake ciki a kasar ta Sham ya kara tsananta, amma yana fatan alheri ga burin warware rikicin ta hanyar siyasa, yace MDD za ta ba da taimako gwagwadon karfinta don cimma wannan nufi.

Dadin dadawa, a wannan rana, ministan harkokin waje na kasar Rasha Sergei Lavrov, ya nuna a birnin Istambul na kasar Turkiya cewa, Rasha na kin amincewa da tsoma baki cikin harkokin kasar Sham ta hanyar daukar matakin soja, kuma yana fatan za a kauracewa daukar matakin soja, a gun taron abokan Sham da za a yi a birnin.

Ban da haka kuma, minsitan tsaron kasar Amurka Chuck Hagel, a wannan rana ya sanar da cewa, Amurka za ta tura ma'aikatan soja kimanin 200 zuwa kasar Jordan, don taimaka mata wajen tsaron bakin iyakar dake tsakanin ta da kasar Sham, da fuskantar barazanar da ake yi mata da makamai masu guba daga kasar Sham. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China