in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangarorin biyu dake rikici a kasar Syria sun keta hakkin dan Adam
2013-02-19 10:47:38 cri
Ran 18 ga wata, hukumar binciken harkokin kare hakkin dan Adam ta kasa da kasa dake kasar Syria ya gabatar wa kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD wani sabon rahoto a birnin Geneva inda ya nuna cewa, cikin shekaru biyu da suka gabata da aka samu rikice-rikice tsakanin sojojin gwamnatin kasar Syria da 'yan adawa, dukkan bangarorin biyu sun gudanar da aikace-aikacen keta hakkin dan Adam.

Rahoton ya nuna cewa, bangarorin biyu dukkansu sun kashe fararen hula da kuma masu shiga rikici yayin da ake cikin yanayin kwanciyar hankali a kasar.

Ya kuma kara da cewa, bangarorin biyu suna da hannu cikin aikace-aikacen bata hakkin yara da suka hada da kisan yara, da kuma yi musu zalunci.

Shugaban kwamitin bincike Paulo Pineiro ya jadadda cewa, kamata ya yi bangarorin biyu dake rikici a kasar Syria su tsayar da dukkan aikace-aikacen tashin hankali tsakaninsu ta hanyar siyasa, kuma a yi wa masu laifin yaki hukunci.

A wannan rana, jakadan kasar Rasha da ke kasar Lebanon Alexander Zasypkin ya bayyana a birnin Beirut cewa, kada a raba kai yayin warware matsalar Syria, sabo da kasar Rasha na ganin cewa, hanyar da ta fi dacewa wajen warware matsalar Syria ita ce a yi shawarwari tsakanin bangarorin daban daban na kasar Syira, kuma wannan hanya za ta iya biyan bukatun jama'ar kasar, na ci gaban kasa cikin yanayin zaman lafiya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China