logo

HAUSA

Hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin tattalin arzikin dijital ta haifar da dimbin sakamako

2024-05-13 20:57:08 CMG Hausa

A shekarun baya, manhajojin wayar salula da kamfanonin Sin suka zuba jari cikinsu na kara samun karbuwa a kasar Najeriya. Wani abokina ya taba gaya min cewa, ya kan yi amfani da Opay wajen tura kudi. Ya ce yadda ake amfani da shi na da sauki, saboda kusan babu wata dakatarwa. Sa’an nan wani aboki ya ambaci APP mai suna Boomplay, ya ce ya kan saurari wakoki a kansa, ganin yadda ake samun dimbin wakokin kasashen Afirka a cikin APP din. To, wadannan misalai sun nuna yadda hadin kan kasashen Afirka da kasar Sin ta fuskar tattalin arzikin dijital da ya shafi fasahohin zamani ya zurfafa.

A wajen taron kulla huldar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a fannonin tattalin arziki da cinikayya, da ya gudana a Nairobi na kasar Kenya, a kwanakin baya, jami’ar Hunan ta kasar Sin, da cibiyar binciken dabarun habaka hadin kan Sin da Afirka kan tattalin arizki da ciniki, sun gabatar da wani rahoto kan hadin kan Sin da Afirka ta fuskar tattalin arzikin dijital, inda suka yi cikakken bayani kan sakamakon da kasashen Afirka da kasar Sin suka samu, a kokarinsu na hadin gwiwa a fannin tattalin arikin dijital, cikin shekarun nan.

Rahoton ya nuna cewa, a fannin gina kayayyakin more rayuwa masu alaka da tattalin arzikin dijital, kasar Sin ta aiwatar da dimbin ayyuka na shimfida wayoyin sadarwa a karkashin teku, wadanda suka hada nahiyar Afirka da sauran nahiyoyi daban daban. Kana kamfanonin kasar Sin sun gina fiye da rabin tashohin wayar salula na kasashen Afirka.

A fannin samar da APP din wayar salula, dimbin kamfanonin hada-hadar kudi na kasar Sin na samar da hidimomin biyan kudi ta wayar salula, da tura kudi tsakanin kasashe, a nahiyar Afirka. Ban da haka, kamfanin Alibaba na kasar Sin ya yi hadin gwiwa tare da gwamnatin kasar Rwanda wajen kafa wani dandalin ciniki mai taken Afnea, wanda ya zama wani dandalin sarin kananan kayayyaki dake da farin jini a gabashin nahiyar Afirka.

Haka zalika, a fannin kirkiro fasahohi, kamfanin Huawei na kasar Sin ya kafa cibiyar adana alkaluma a kasar Afirka ta Kudu, wadda ta samar da hidimomi masu inganci da tsaro. Yayin da kamfanonin Sin ke hadin kai tare da kasashen Masar da Aljeriya, dai dai sauransu, wajen kafa cibiyar kula da ayyukan taurarin dan Adam ta kasar Sin da kasashen Afirka. Ban da haka, a fannin bayar da horo, Sin da kasashen Afirka sun kafa dimbin dandalin samar da ilimi da musayar fasahohi, karkashin hadin gwiwarsu.

Wadannan abubuwa suna cikin dimbin sakamakon da aka ambata, cikin rahoton da aka gabatar, dangane da hadin gwiwar Sin da Afirka, ta fuskar tattalin arziki na dijital.

Sai dai me ya sa ake samun wannan yanayi mai armashi a hadin gwiwar Sin da Afirka a kokarinsu na raya tattalin arzikin dijital?

Da farko, an samu damar raya tattalin arzikin dijital a kasashen Afirka yanzu.

A fannin manufofi, kungiyar kasashen Afirka AU ta zartas da ajandar aiki ta shekarar 2063, inda ta saka burin mayar da nahiyar Afirka yankin tattalin arzikin dijital mai tsarin bai daya. Kana mambobin kungiyar sun dora muhimmanci kan raya tattalin arzikin dijital a cikin gida. Misali, kasar Najeriya ta tsara shirin kara saurin yanar gizo ko Internet, da sanya ta shafar karin mutane. Ban da haka, a fannin muhallin kasuwanci, habakar biranen kasashen Afirka cikin sauri ta samar da kasuwanni ga hidimomi na dijital, kana kafuwar yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar Afirka ta ba da damar inganta hadin gwiwar kasashen Afirka ta fuskar tattalin arzikin dijital.

Na biyu, shi ne, fasahohin kasar Sin a fannin yanar gizo su ne a kan gaba a duniya.

An kammala aikin gina kayayyakin more rayuwa masu alaka da fasahohin sadarwa mafi girma a duniya, a kasar ta Sin, ta yadda ko a cikin kauyukan kasar ma, ana samun ingantaccen tsarin sadarwa. Ban da haka, kasar ita ta fara rungumar fasahar sadarwa mai inganci ta 5G, inda a karshen shekarar 2023, yawan al’ummar kasar masu wayoyin salula dake aiki da 5G ya kai miliyan 805. Ban da haka, kasar Sin ta kware a fannin kirkirar sabbin fasahohi, abin da ya sa ta kan gaba a duniya a fannonin mallakar fasahohi masu alaka da na’urorin kwaikwayon tunanin dan Adam, da aikin tsara karamin kayan latironi na Chip, da dai sauransu.

Kana dalili na uku shi ne, akidar kasar Sin ta fuskar hadin kai tare da kasashen Afirka bisa gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da samar da sakamako na zahiri, ta sa kasar yarda da gabatar da ingantattun fasahohi, da damammakin raya kasa, ga bangarorin Afirka.

Cikin shawarar kafa al’umma mai makomar bai daya a fannin yanar gizo bisa hadin gwiwar Sin da Afirka, da kasar Sin ta gabatar, kasar ta yi alkawarin taimakawa kasashen Afirka wajen gina kayayyakin aikin sadarwa, da kula da yanar gizo, da sayar da kayayyaki ga kasuwannin Sin ta hanyar cinikin yanar gizo, da kuma rage talauci ta hanyar amfani da fasahohin zamani, da sauransu.

A lokacin baya, mutane kalilan na kasashen Afirka ne suke da damar duba shafukan yanar gizo ko Internet. Amma zuwa yanzu, ci gaban fasahohi ya sa dimbin mazauna yankunan karkara na nahiyar Afirka na iya kallon shafukan Internet ta wayar salula, don more damammakin sadarwa da samun bayanai. Ta haka za mu iya ganin yadda fasahohin zamani ke haifar da rayuwa mai inganci a nahiyar Afirka. Sa’an nan abun da kasar Sin ke yi yanzu, shi ne kara saurin shigar da ingantattun fasahohi cikin nahiyar Afirka, ta yadda za a ba dukkan bangarorin Sin da Afirka damar amfanar juna, da samun ci gaba na bai daya. (Bello Wang)