logo

HAUSA

Tawagar jami’an wanzar da zaman lafiya ta Sin ta bayar da gudunmuwa ga DRC

2024-04-30 20:58:12 CMG Hausa

Tawagar jami’an kasar Sin dake cikin tawagar shirin wanzar da zaman lafiya na MDD (MONUSCO), ta bayar da gudunmuwar kayayyakin aikin injiniya da injuna da kayayyakin kiwon lafiya, ga gwamnatin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo DRC a jiya Litinin.

An gudanar da bikin mika kayayyakin ne a wajen birnin Bukavu, hedkwatar lardin South Kivu dake gabashin kasar. (Fa’iza Mustapha)