logo

HAUSA

Xi ya yi rangadi a birnin Chongqing dake kudu maso yammacin kasar Sin

2024-04-23 14:25:26 CMG Hausa

Shugaban kasar Sin kuma sakatare janar na kwamitin kolin JKS, Xi Jinping, ya yi rangadi a birnin Chongqing dake kudu maso yammacin kasar, daga jiya Litinin zuwa yau Talata.

Yayin rangadin, Xi Jinping ya kai ziyarar cibiyar jigilar kayayyaki ta kasa da kasa, da unguwar mazauna dake yankin Jiulongpo, da kuma cibiyar tafiyar da harkokin birnin ta zamani.

Ya kuma gano kokarin da gwamnatin birnin ke yi wajen gaggauta raya sabuwar cibiyar cinikayya daga kan tudu zuwa teku ta kasa da kasa dake yammacin kasar, da aiwatar da ayyukan sabunta birnin, da tabbatar da kyautata rayuwar jama’a, da ma yunkurin zamanantar da tsarin tafiyar da harkokin birnin. (Fa’iza Mustapha)