logo

HAUSA

Sin ta kira taron tattauna kan rahoton gwamnati

2024-02-29 19:35:31 CGTN HAUSA

 

A yau Alhamis ne ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ya kira wani taro don tattauna rahoton ayyukan gwamnatin kasar, wanda majalisar gudanarwar kasar ke shirya gabatarwa, ga taro karo na biyu na babban taron jama’ar kasar Sin karo na 14. Kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ne ya jagoranci taron.

A gun taron, an bayyana cewa, a cikin shekarar da ta gabata, an cimma burin raya tattalin arziki da al’umma a kasar Sin, inda aka tabbatar da samun bunkasuwa mai inganci yadda ya kamata.

A shekarar bana kuma, Sin za ta karfafa da inganta yanayi mai kyau na farfadowar tattalin arziki, ta yadda za a habaka bunkasuwar tattalin arziki mai inganci. (Amina Xu)